Zan iya auren talaka – ‘Maryam Labarina’

Описание к видео Zan iya auren talaka – ‘Maryam Labarina’

Matashiyar tauraruwar finafinan Kannywood Fatima Hussaini Abbas ta ce halayenta a cikin shirin Labarina su ne kusan halayenta na zahiri domin kuwa “ba na soyayya domin kudi”.
A hirarta da TRT Afrika Hausa, tauraruwar wadda aka fi sani da Maryam a Labarina, ta ce za ta iya auren talaka idan har tana kaunarsa.
“Ba wai ina nufin ihsani ba shi da dadi ba ne. Amma ba na son mutane don abin da suka mallaka ko abin da za su ba ni.”
Ta kara da cewa halaye na kwarai su ne ginshikin soyayya ba kudi ba.
“Idan talaka ya fito ya ce zai aure ni, idan har ina sonsa sannan akwai fahimtar juna tsakanina da shi, babu abin da zai hana ni aurensa. Saboda wasu sai sun yi auren Allah yake azurta su,” in ji ta.

  / trtafrikaha  
  / trtafrikaha  
  / trtafrikaha  

Комментарии

Информация по комментариям в разработке